Yayin da al'ummar duniya ke ƙaruwa, buƙatar ruwa mai kyau da tsafta kuma mai sauki na ƙaruwa ita ma, abin da ke sa matsi da raguwar ruwan da ake da shi. Wannan shi ne ake kira ''matsin ruwa''.
Zuwa shekara ta 2025, rabin al'ummar duniya za su kasance suna rayuwa a yankunan da ke fama da matsalar matsin ruwa, kmar yada Hukumar Lafiya ta Duniya ta bayyana.
Ba za a iya ci gaba da samar da ruwa mai daɗi ba daidai da buƙatar duniya da ke karuwa ba. Ba a samun ruwa daidai-wa-daida a fadin duniya, kuma zai kasance da matukar wuya a riƙa samo ruwa mai daɗi kuma zai yi tsada a rika safararsa.
Ƙaruwar jama'a da bunkasar birane da sauyin yanayi na daga cikin abubuwan da ke haddasa ƙarancin, ta hanyar rashin ruwan ko kuma gurɓata hanyoyin da ake da su na samun ruwan.
Zuwa shekara 30 nan gaba an yi hasashen yawan al'ummar Afirka zai ninka biyu zuwa biliyan 2 da rabi in ji Ƙungiyar Hadin kan Tattalin Arziki da Ci-gaba (OECD).
Tuni daman rabin al'ummar Afirka na zaune ne a birane, kuma sama da rabinsu suna zaune ne a unguwanni na talakawa.
Ƙwararru sun yi gargagaɗin cewa matukar ba a ɗauki mataki ba mutane sama da miliyan ɗari daya a birane za su fuskanci matsanancin ƙarancin ruwa.
Bayani daga: Rabe-raben yanayi na ƙungiyar Köppen-Geiger
Afirka ce nahiya mafi ƙarancin ruwa a duniya. Kusan biyu bisa uku na sararinta ko dai mai karancin ruwa ne ko kusa da haka.
Ɗaya daga cikin mutum uku a yankin Afirka kudu da hamadar Sahara na rayuwa ne a wurin da ake fama da ƙarancin ruwa.
Eritrea da Botswana na daga cikin ƙasashen Afirka da dama da ke fama da matsalar ruwa.
Bayani daga: Rabe-raben yanayi na ƙungiyar Köppen-Geiger
Afirka ce nahiya mafi ƙarancin ruwa a duniya. Kusan biyu bisa uku na sararinta ko dai mai karancin ruwa ne ko kusa da haka.
Bayani daga: Rabe-raben yanayi na ƙungiyar Köppen-Geiger
Ɗaya daga cikin mutum uku a yankin Afirka kudu da hamadar Sahara na rayuwa ne a wurin da ake fama da ƙarancin ruwa.
Daga: OECD 2021
Eritrea da Botswana na daga cikin ƙasashen Afirka da dama da ke fama da matsalar ruwa.
Sauyin yanayi na haddasa yanayi da ba za a iya hasashe ba da ya hada da fari da ambaliya. Kyawun ruwan da ake samu daga ƙarkashin ƙasa ya ragu a yankuna da yawa
Ana asarar miliyoyin ranaku na aiki da nazari a kowa ce sheakara saboda rashin lafiya wadda rashin ruwa ko rashin kyawunsa ke haddasawa.
Duba manyan ƙalublen samun ruwa a ƙasarku
Manyan matsaloli da ƙalubale sun haɗa da: Mene ne matsayin ruwa mai kyau da tsafta a nan?
Source:
A wane hali ake ciki kan batun samun tsaftataccen ruwa da tsaftar muhalli a
Ta yaya ake ƙokarin cimma burukan samun ruwa mai kyau da tsafta?
A cikin shekara ashirin da ta gabata an samu ci gaba sosai wajen samar da ruwan famfo mai sauki da tsafta a faɗin Afirka
Amma duk da haka har yanzu akwai manyan matsaloli
Ruwa mai kyau shi ne wanda ake samu cikin sauƙi wanda kuma bai gurɓata ba. Kashin yawan mutanen birni da ke samun ruwa mai kyau a Afirka ya kama daga kashi 9 cikin ɗari a Laberiya zuwa kashi 99 cikin ɗari a Afirka ta Kudu, kamar yadda Hukumar lafiya ta Duniya, WHO da Asusun yara na Majalisar Ɗinkin Duniya, UNICEF suka bayyana.
A 2015 Babban taron Majalisar Ɗinkin Duniya ya ƙuduri aniyar tabbatar da samar da ruwa da tsafta ga kowa a matsayin ɗaya daga cikin buruka17 masu ɗorewa na ci gaba (SDGs)
Ana kirn wannan SDG 6
Djibouti da Moroko da namibia da Masar na daga cikin ƙasashen da ka yi hasashen za su iya fuskantar tsananin ƙarancin ruwa
To amma kum dukkanin ƙasashen Afirka na fuskantar manyan ƙalubale wjen cimma burin na SDG 6
Wani nazari da aka yi a 2019 ya gano wasu ƙasashen Afirka na ƙoƙari, amma a rabinsu babu wani ci gaba.
Matakan na mayar da hankali ne a kan ɓangarori uku: gyara ruwan da amfani da shi da kuma da kuma sake amfani da ruwan da aka riga aka yi amfani da shi; inganta ayyukan gona; da zuba jari a ayyukan injiniya da ake amfani da kankare da ƙarafuna, waɗanda suka dogara ga tsirrai da sauran halittu da muhallinsu.
Ainahin bayanan an samo su ne daga rahotanni da makaloli da ayyukan bincike da ƙungiyoyi da suka haɗa da Hukumar Lafiya ta Duniya (WHO) da Bankin Duniya da Ƙungiyar Hadin kan Tattalin Arziki da Ci-gaba (OECD) da Cibiyar Bayanai ta Duniya (WRI, da gwamnatocin yankun da kuma na tarayya.Akwai kuma wasu gomman kafofi da aka amince da su da ake amfani da su wajen samun bayanan da za a iya ƙarawa a kan bayanan da waɗancan manyan ƙungiyoyi ke samarwa. Ana yin hakan ne domin a tabbatar ba a bar wani giɓi ba a cikin manyan bayanan kuma a tabbatar an wakilci yawancin ƙasashen Afirka.
Ƙungiyoyin da suka tattar bayanan sun mayar da hankali ne kan inda suke da jami'aiinda kuma ake da bayanai da aka riga aka samar.Domin tabbatar da an sanya ƙasashe yadda ya kamata, an sa ƙarin bayanai na birni da kasa daga bincike da rahotanni da maƙaloli masu inganci domin cike wani giɓin.
"Anthony Irungu da Chakuchanya Harawa ne suka hada da rubutawa. Muthoni Muchiri da Princess I. Abumere ne suka tsara aikin samar da bayanan. Purity Birir da Theo Okafor da kuma Zoë Thomas ne suka fadada. Millie Wachira ta tsara. Gidauniyar Bill & Melinda Gates Foundation ce ta samar da kudin aikin. "